Majalisar wakilan Najeriya ta bukaci a sanya dokar ta-baci a yankin Arewa maso Gabashin kasar, sakamakon ta'azzarar matsalar rashin tsaro. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ganin farin jinin da Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriyar ke da shi ya fara dishewa, bayan da ya sha ihu a Maiduguri fadar gwamnatin jihar Borno.