1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Buhari ya rantsar da ministocinsa

Mohammad Nasiru Awal AH
August 21, 2019

Shugaba Buhari na Najeriya ya rantsar da wakilan majalisar ministocinsa inda ya nada Timipre Silva mukamin karamin ministan mai.

https://p.dw.com/p/3OHJZ
Muhammadu Buhari
Hoto: DW/I. U. Jaalo

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya a wannan Laraba ya rantsar da membobin majalisar ministocinsa inda ya nada sabon mukamin karamin ministan albarkatun mai a majalisar mai ministoci 43.

Har yanzu dai Shugaba Buharin ne zai ci gaba da rike mukamin ministan mai kamar yadda yake tun a  wa'adin mulkinsa na farko, sai dai ya nada Timipre Silva a matsayin ministan kasa na albarkatun mai.

Shi dai Silva da ke zama tsohon gwamnan jihar Bayelsa, ya maye gurbin Emmanuel Kachikwu da ya kasance wakilin Najerya a kungiyar OPEC.

Zainab Ahmed za ta ci gaba da rike mukaminta na ministar kudi.