1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya ta yi bayani kan kisar 'yan hijira

July 22, 2017

Rundunar soji a Najeriya ta fito da wasu bayanai dangane da kisan sakaci da ta yi wa sama da 'yan gudun hijira 100 a kauyen Rann da ke arewa maso gabashin kasar a watannin da suka gabata.

https://p.dw.com/p/2gzz4
Nigeria Luftangriff auf Flüchtlingslager
Hoto: Reuters/MSF

Rundunar mayakan saman kasar ta ce babban dalilin faruwar lamarin, shi ne na rashin shaata sansanin 'yan hijiran cikin taswira ta yadda za su fahimta. Wasu hotunan bidiyo da taurarun dan adam ya nuno, ya bayyana wani taron jama'ar da sojin basu san da su ba, da kuma suka yi zaton mayakan Boko Haram ne da suke kwantonsu a dazukan yankin.

Harin na Bam dai ya halaka galibi mata ne da kananan yara gami da wasu jami'an agaji na Red Cross. Kwamandojin yaki a yankin sun ce hakan, kuskure ne irin na yaki da ba so shi ba.