1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya za ta kara kudi a fannin tsaro

Zulaiha Abubakar
December 14, 2017

Babban akantan kasar ya sanar da cewar a asusun rarar man fetur na Najeriyar na makare da zunzurutun kudi sama da dala biliyan biyu

https://p.dw.com/p/2pOwQ
Zentralbank von Nigeria

 

Gwamnan jihar Edo Godwin Obaseki ya shaida wa manema labarai a Abuja babban birnin kasar cewar, yabawar da gwamnonin kasar suka yi  da irin cigaban da aka samu a bangaren yaki da Ta'addanci, shi ne dalilinsu na amincewa da a fidda dala biliyan daya daga asusun don cigaba da yakar ayyukan ta'addanci a kasar.

An  dai tsayar da lokacin sabon zaben shugaban kasa da gwamnaonin Najeriya a watan Fabarairu zuwa watan Maris na shekara ta 2019,lamarin da tarihin ya nuna shike zaburar da 'yan siyasa wajen satar kudaden kasar.