1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Masu garkuwa da mutane sun addabi jama'a

April 4, 2019

Wannan al'amari dai da farko an dan samu saukinsa amma kuma daga baya-baya nan lamarin ya kara lallacewa. A kasa da mako daya kawai goman mutane ne aka sace tsakanin hanyar Kaduna zuwa Abuja.

https://p.dw.com/p/3GBrM
Bombenexplosion Polizei in Nigeria
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Wannan al'amari dai da farko an dan samu saukinsa amma kuma daga baya-baya nan lamarin ya kara lallacewa. A kasa da mako dai kawai sama da mutane guda 30 aka sace tsakanin hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Hanyar jirgin kasa ta fi tabbas fiye da ta mota saboda masu yin sata da yin garkuwa jama'a

Nigeria Eröffnung Eisenbahnlinie zwischen Abuja und Kaduna
Hoto: DW/U. Musa

Darurruwan jama'ar ne a Jihar Kauna ta Najeriya ke yin tururruwar zuwa daukar jirgin kasa daga Kaduna zuwa Abuja domin kaucewa masu yin fashi a kan hanyoyin mota. Wadanda ke satar mutane tare da yin garkuwa da su domin neman kudaden fansa. Duk da irin kokarin da 'yan sanda suke yi na ciwo kan al'amarin har yanzu da sauran rina a kaba.