1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

NATO na kara daukan matakan inganta tsaro a Iraki

Zulaiha Abubakar
February 15, 2018

Kungiyar tsaro ta NATO ta dauki aniyar fadada ayyukan sojojin kungiyar zuwa kasar Iraki,a cikin shirye-shiryen farfado da kasar ta hanyar ginin makarantu da kuma sansanin horas da aikin sojoji.

https://p.dw.com/p/2slh0
Nato-Hauptquartier in Brüssel
Hoto: picture-alliance/dpa/K. Nietfeld

Sakataren kungiyar ta tsaro ta NATO Jens Stoltenberg ya sanar da cewar kungiyar za ta yi nasara, sai dai bai bayyana in da za a gudanar da ayyukan ba da kuma adadin jami'an tsaron kungiyar da za su gabatar da ayyukan ba kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AFP ya sanar.