1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Firaministan Isra'ila zai karbe wuraren yahudawa bayan zabe

Abdoulaye Mamane Amadou
April 7, 2019

A kasar Isra'ila Firaminista Benjamin Netanyahu ya yi alkawalin karbe wuraren da yahudawa suka mamaye idan ya sake ci zaben 'yan majalisa.

https://p.dw.com/p/3GQCA
Russlands Präsident Putin trifft sich mit dem israelischen Präsidenten Benjamin Netanjahu
Hoto: picture-alliance/ZUMAPRESS.com/A. Druzhinin

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana aniyarsa ta karbe wuraren yahudawa 'yan share wuri zauna idan ya sake lashe zaben majalisar dokoki da ake shirin gudanarwa a kasar a makon gobe.

Tun a shekarun 1967 ne yahudawa 'yan kama wuri zauna suka mamaye yankin na Falastinu da Firaminitsan Isra'ila Netanyahu ke cewa zai karbe duba, matakin ya sha samun kakkausar bisa sabawa dokokin kasa da kasa.

A wata hira da kafar yada labarun Israila Firaminsta Netanyahu ya ce zai tabbatar da 'yancin Isra'ila ba tare da bambamci tsakanin 'yan kasar ba.