1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar na fiskantar matsalolin tsaro

September 20, 2013

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta mayar da martani kan rahoton da ya bayyana cewa, kasar na fiskantar barazanar tsaro daga kasashe makwabta.

https://p.dw.com/p/19lNl
This photo taken on June 1, 2013, shows soldiers standing guard at the entrance of the main prison in Niamey. Inmates in Niamey's main prison killed two guards on June 1, officials said, a week after twin suicide bombings claimed 20 lives in the west African country. Three inmates charged with terrorist offences tried to had break out of the prison, prosecutor Ibrahim Wazir Moussa said on state television. AFP PHOTO / STRINGER (Photo credit should read STR/AFP/Getty Images)
Jami'an tsaron Nijar, bayan wani harin a gidan yarin YamaiHoto: STR/AFP/Getty Images

Cikin wani rahoto na baya-bayan nan da ta fitar, kungiyar kare afkuwar rikice-rikice mai suna Crisis Group ta bayyana cewa, sanadiyyar tabarbarewar tsaro a yankunan Janhuriyyar Nijar, ya sanya gwamnatin kasar bayar da fifikon kashe kudade ta fuskar tsaro fiye da sauran fannonin ci gaban rayuwa.

Crisis Group ta bayar da misali da tagwayen hare-haren da aka kai a birnin Agadez da wanda aka kai ma'aikatar hako ma'adinan yuraniun dake yankin Arlit cikin watan Mayu. Har ila yau da wanda aka kai kan gidan yarin kasar da ke birnin Yamai a ranar daya ga watan Yuni, al'amarin da manazarta da su ka hadar da Ibrahim Bah na kungiyar Crisis Group ke ganin hakan ya bayyana karara irin barazanar tsaro da kasar ke fuskanta.

Anführer der Opposition in Niger English: Mahamadou Issoufou (VOA photo- N. Colombant) 4 December 2004(2004-12-04) Source http://www.voanews.com/english/archive/2004-12/Opposition-In-Niger-Cries-Foul.cfm Author VOA photo- N. Colombant
Mahamadou Issoufou, shugaban kasar NijarHoto: N. Colombant

A cewar kungiyar barazanar dai na zuwa ne daga makobtan kasashe da suka hadar da arewacin Mali mai fama da kungiyoyin jahadi, da Boko Haram a arewacin Najeria, da ke tsallakowa domin tserewa harin dakarun Najeriyar. Ibrahim Bah yace wanann barazanar kadai ta ishi jefa Nijar cikin fargabar shiga tsakiyar kungiyoyin 'yan ta'adda.

Da yake mayar da martani akan wannan rahoto, ministan sadarwa Jamhuriyar Nijar Malam Yahouza Sadissou, yace hare-haren da aka samu a wasu yankunan Nijar baya nufin gwamnati ta yi sako-sako ga matsalar tsaro.

Yahouza Sadissou.jpg Bild für die DW-Radio/Redaktion Seite
Yahouza Sadissou, ministan sadarwan kasar NijarHoto: DW

Ministan ya ce, dukkanin matakan da ake dauka ba za ka ce ka samu nasara dari bisa dari ba, abin da ya faru a Agadez da birnin Yamai bai taka kara ya karya ba, in da an kwatanta da tashe-tashen hankulan da kasashe makwabta ke fama da shi. Babban abin da gwamanti ta sa a gaba shi ne na ganin ta kare al'ummarta, ba zai hana a samu wani rikici da bai taka kara ya karya ba.

Kungiyar ta Crisis Group, ta kuma yi tsokaci game da yadda gwamnatin Nijar ta ba da wani fifiko wajen kashe kasafin kudin kasar ga tsaro, fiye da sauren fanonin ci-gaban rayuwar al'umma. Matakin da Mininstan sadarwa Yahouza Sadissou ke cewa, dole ne a yi wa demokradiyyar kasar uzuri, tun da ta na kan tafarkin koyo ne ba waa wani kwari ta yi ba.

###ACHTUNG! NUR ZUR MIT DEM COPYRIGHTINHABER ABGESPROCHENEN BERICHTERSTATTUNG VERWENDEN### Resource ID 71187 Access Open Region West Africa Country Niger SCO 1.1 Food & Income Security Area of Work Disaster Risk Reduction Campaign Climate Change, GROW Humanitarian Crisis Drought, Food Crisis Classification Humanitarian Date 08 March 12 Credit Fatoumata DIABATE Copyright Fatoumata Diabate Caption Cash for wortk to build the half-moon structures on bare soil. The structures are designed to preserve the rain water when it next rains, refilling the water table and encouraging vegetation to grow back. Programme Information Cash for work programme in the village of Gobro, Departement of Tibiri, region of Dosso, 1000 km east from Niamey The project is run in partnership with World Food Programme and Oxfam's partner NGO Mooriben. In exchange for cash (1000 XOF per day), beneficiaries are investing in the recuperation of land for agriculture. Schemes providing cash in exchange for work on community projects are one way Oxfam and partners keep food accessible for the most vulnerable while helping to protect markets. Oxfam invests in 'cash-for-work' projects and other cash initiatives, so that people have access to food on markets and markets are not distorted by food aid. In Niger, even in time of food shortage, the issue is more often related to access to food because of deep poverty and lack of financial resources or high prices, rather than to the unavailability of food on the market. In response to the current crisis, Oxfam and its partners are planning to help 450,000 people with vital aid such as food, cash, support to livestock, water, sanitation and hygiene promotion campaigns. In total, more than million people are facing a severe risk of food crisis in Niger. Specifically, in response to the influx of 30,000+ people from Mali, Oxfam and its partners are working to respond to the needs of refugees and host communities in the following sectors: food security, water, hygiene and sanitation, education and protection against gender-based violence. --------- Oxfam-Einverständniserklärung zugeliefert von Anne Le Touzé
Yanayin noma a wasu yankunan kasar NijarHoto: Fatoumata Diabate/Oxfam

Har ila yau rahoton kungiyar kare afkuwar rikice-rikice, ya ce yanayin siyasar da ake ciki da ya baiwa gwamnatin neman hadin gwiwar jamiyyun adawa domin kafa gwamnatin hadin kai, ba komai ya ke nunawa ba illa bayyanar kamari da matasalar kasar ta yi. Akan wannan ma dai ministan Sadarwa ya danganta rikice rikicen na siyasa da abin da demokaradiyya ta gada.

A karshen wannan rahoto kungiyar ta Crisis Group ta yi kira ga shugaban Jamhuriyar ta Nijar, Mouhamadou Issoufou da ya matsa kaimi, domin cika alkawuran da ya daukar wa talakawa.

Mawallafi: Youssoufou Abdoulaye

Edita: Usman Shehu Usman

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani