1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Pakistan: Cinkoso jama'a ya janyo asarar rayuka

Abdourahamane Hassane
March 31, 2023

Akalla mutane tara ne suka mutu a wani turmutsitsin da ya barke a birnin Karachi da ke kudancin Pakistan,yayin da jama'a suka garzaya zuwa wata masana'anta da aka shirya rabon sadaka na azumin Ramadan.

https://p.dw.com/p/4PZgN
Pakistan Krankenhaus in Karatschi bei einer Massenpanik während einer Ramadan-Almosenverteilung
Hoto: ASIF HASSAN/AFP

Turmutsitsin ya faru ne a lokacin da mata mabukata da ‘ya'yansu suka cincirindo a masanantar.inda cinkosso jama'a ya yi yawa.Yanhzu haka an kai gawarwakin mata shida da yara uku zuwa asibiti in ji kakakin 'yan sanda birnin na karashi Muhammad Farukh.