1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin kula da talakawa shine matsalar Najeriya

Usman ShehuNovember 14, 2012

Wasu gwamnonin a Arewacin Najeriya sun bayyana cewa muddi ana son zaman lafiya mai ɗorewa a yankin, dole shugabanni su kusanci talakawa

https://p.dw.com/p/16jNf
Kashim Shettima, Gouverneur von Borno State, Nigeria Usman Shehu, 15.06.2011, Maiduguri / Nigeria
Kashim Shettima, Gwamnan jihar BornoHoto: DW

Gwamna Kashim Shetima na jihar Borno dake Arewa maso gabashin Najeriya mai fama da tashin hankalin da ake dangantawa da Boko Haram ya yi gargadin cewa matukar gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya ba su yi adalci wa talakawan su gami da jan su a jiki ba, to kuwa mulki yankunan su zai iya gagarar su nan gaba.

Gwamnan wanda yake bayanin kan hanoyin da za'a magance matsalar Boko Haram, yace tashe-tashen hankulan da ake fuskanta a yankunan Arewacin Najeriya suna da nasaba da yadda shugabannin yankin suka yi watsi da talakawan su, inda suka bige da tara kudade don gudun talauci.

Markt in Borno-State, Nigeria. Wer hat das Bild gemacht/Fotograf?: Katrin Gänsler Wann wurde das Bild gemacht?: 15. Februar 2008 Wo wurde das Bild aufgenommen?: Borno-State, Nigeria
Nigeria wani mai tallan shayi a MaiduguriHoto: Katrin Gänsler

Yace kamata ya yi gwamnonin da sauran wadanda aka zaba su cika alkawuran da su ka yi wa talakawa maimakon nuna mulki ko karfin iko ko kuma sama da fadi tare da barin talakawan cikin kangin talauci da rashin aiki. Wannan a cewar sa ba zai haifar da alheri ba kuma masu mulkin za su iya rasa shi anan gaba, ganin talakawa sun fara gane abinda duniya ke ciki.

Masu fashin baki da talakawan kasar sun gaskata wannan furuci na gwamnan inda suka bukaci masu fada aji a yankin su rungumi talakawa ba tare da nuna kyama ba, in suna so su tsira da mutunci a idon talakawan. Dr Sadiq Umar Abubakar wani mai fashin baki ne kan harkokin yau da kullum ya gaskata wannan gargadi na gwamnan jihar Borno.

A photograph made available 23 January 2012 shows Nigerian President Goodluck Jonathan (C) addressing the Emir of Kano (R) during a visit to his palace following the bomb blasts in Kano, northern Nigeria, 22 January 2012. A series of attacks apparently orchestrated by Islamist militants of the 'Boko Haram' group in the northern Nigerian city of Kano on 20 January 2012 have killed more than 160 people according to reports. More than 10 locally made explosive devices were found in abandoned vehicles in the city. A call to stop the violence has been issued by the Kano state government. EPA/STR EPA/STR
Goodluck Jonathan da sarkin Kano Ado BayeroHoto: picture-alliance/dpa

Wannan ya sa kungiyoyin matasa suke cewa ba za ta sabu ba a wannan karon duk wanda ya guji talakawa to ba za su bari a sake zabar sa ba, lamarin da ake ganin yana gaskata maganar gwamnan jihar Bornon ne. Saboda haka ne ma matasan suka bukaci gwamnonin da sauran zababbu wakilai da su tabbatar sun yi adalci tare da yin ayyukan da za su kyautata rayuwar talakawa, ta hakane kawai za'a magance matsaloli da ake fuskanta a Arewacin Najeriya.

Malam Ibrahim Yusuf wanda aka fi sani da Three Thousand daya daga cikin shugabannin matasan Arewacin Najeriya ne masu fafutukar tabbatar da dalci wa al'umma. Shi ma ya go yi bayan matakin kusantar masu mulki ga wadanda suke mulka, muddin ana son tsaman lafiya.

A baya ma dai kungiyoyin fararen hula da talakawa sun yi irin wannan gargadi to amma babu wani canji na azo a gani, musamman a yankin Arewacin Najeriya, inda zababbun shugabanni ke buya daga ganin talakawan su har sai lokacin zabe ya karato suke bayyana.

Mawallafi: Al-Amin Sulaiman Muhammed

Edita: Usman Shehu Usman