1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin tabbas kan taron Siriya

October 21, 2013

Harin kunar bakin wake ya hallaka mutane 30 a Siriya yayin da aka kasa sanya ranar gudanar da taron neman zaman lafiyar kasar.

https://p.dw.com/p/1A2y2
Hoto: Reuters

Akwai rashin tabbas kan gudanar da taro neman kawo karshen rikicin da ke faruwa a kasar Siriya. Yayin da kungiyar Kasashen Larabawa ke cewa za a gudanar da taron cikin watan gobe na Nowamba, mai shiga tsakani kan rikicin a madadin Majalisar Dinkin Duniya da kungiyar kasashen Larabawa Lakhdar Brahimi ya ce, babu ranar da aka saka na taron da zai guda a birnin Geneva na kasar Switzerland.

A kasar ta Siriya dai, wani harin kunar bakin wake da aka kai da babbar motar daukan kaya ya yi sanadiyar hallaka mutane 30, sannan wasu masu yawa suka samu raunika a garin Hama.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Mohammad Nasiru Awal