1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikici a Taraba ya jawo salwantar rayuka

June 15, 2014

Rahotanni daga kudancin jihar Taraba a arewacin Najeriya na cewar mutane sama da 30 ne suka mutu a garuruwan Wukari da kuma Ibbi sakamakon wani tashin hankali.

https://p.dw.com/p/1CImI
Symbolbild Gewalt in Nigeria
Hoto: SEYLLOU DIALLO/AFP/Getty Images

Tashin hankalin dai kamar yanda shaidu suka tabbatar ya samo tushensa ne bayan da aka zargi matasan kabilar Jukun da lalata wuraren sayar da wayoyin sadarwa mallakin Hausa-Fulani mazauna garin, yayin kuma da su Hausawan suka nemi dalili, sai fada ya kaure.

A zantawarsa da Wakilinmu na Yolan jihar Adamawa Muntaqa Ahiwa, wani mutum da ya shaida faruwar abin ya ce ya ga gawawwaki da yawa kana an kone gidaje da dama sakamakon barkewar rikicin.

Yankin kudancin Taraba dai yanki ne da ya yi kaurin suna wajen samun rigingimun addini da na kabilaci, rigingimun da ke zama sanadin asarar rayuka da dukiyoyi.

Mawallafi: Muntaqa Ahiwa/Ahmed Salisu
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe