1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin gabacin Kongo ya dauki sabon salo

August 30, 2013

Baya ga hare-haren da sojojin Majalisar Dinkin Duniya ke kaiwa a kan 'yan tawayen M23, ana kuma kai farmaki a tsallaken kan iyakar Kongo da Ruwanda.

https://p.dw.com/p/19Z23
A child stands in front of Indian soldiers of the UN mission in the Democratic Republic of Congo (MONUSCO) driving an armoured vehicle at the border zone in Kagnaruchinya, 7 km north of Goma, on June 2, 2013. The M23 rebellion -- launched by Tutsi former soldiers who mutinied in April 2012 -- is the latest in years of violence that have ravaged the vast central African country's mineral-rich east. A peace deal signed in February by 11 regional countries had brought relative calm until it was broken in the three days leading up to Ban's visit. The two sides stopped fighting while the UN leader toured the flashpoint city of Goma. AFP PHOTO/Junior D. Kannah (Photo credit should read Junior D. Kannah/AFP/Getty Images) Erstellt am: 02 Jun 2013
Hoto: Junior D. Kannah/AFP/Getty Images

Bari mu fara da jaridar Die Tageszeitung wadda a babban labarinta mai taken gumurzu mai hadari ta mayar da hankali a kan Kongo tana mai cewa ba hare-haren sojojin Majalisar Dinkin Duniya a kan 'yan tawaye kadai ke karuwa ba, a'a ana kuma kai farmaki na bindigogi atileri a tsallaken kan iyaka, inda rayuka suka salwanta a Ruwanda sannan sai ta ci gaba kamar haka.

"Wannan shi ne fada mafi muni da aka fuskanta a Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo cikin shekaru da dama. Da alikoftocin yaki na kasar Ukrain da bindigogin atileri na kasar Tanzaniya da sojojin kundun bala na Afirka ta Kudu tawagar Majalisar Dinkin Duniya a Kongo wato Manusco ta taimaka wa sojojin kasa na Kongo a farmakin da suka kai wa 'yan tawayen kungiyar M23 a birnin Goma. An kashe sojan Tanzaniya daya sannan wani sojan Afirka ta Kudu ya samu rauni, amma ba wanda ya kirga sojojin Kongo da fadan ya rutsa da su. A karon farko cikin wannan rikici an samu salwantar rayuka da wadanda suka jikkata a garin Gisenyi dake bangaren Ruwanda na kan iyakar kasashen biyu. Sannan su kuma sojojin Kongo sun sanar ta shafin intanet cewa a hukumance yanzu Ruwanda ta kutsa cikin Kongon don tallafa wa kungiyar M23. Sai dai mazauna a Goma ba su tabbatar da wannan zargi ba. Yanzu haka yankin kan iyakar ya zama wani fagen daga inda gwamnatocin Kongo da Ruwanda ke zargin juna da laifin tabarbaewar halin da ake ciki."

Zabe ka iya guba ga demokradiyya

A picture taken on August 11, 2013 shows a ballot paper with pictures of the two presidential candidates, former prime minister Ibrahim Boubacar Keita (L) and ex-finance minister Soumaila Cisse, at the Malian embassy in Paris during the Malian presidential elections. Malians go to the polls today for a president expected to usher in a new era of peace and democracy in the first election since a military coup upended one of the region's most stable democracies. AFP PHOTO / KENZO TRIBOUILLARD (Photo credit should read KENZO TRIBOUILLARD/AFP/Getty Images)
Hoto: Kenzo Tribouillard/AFP/Getty Images

Ita kuwa a sharhinta jaridar Neue Zürcher Zeitung tsokaci ta yi game da zabe da kuma damokradiyya a Afirka tana mai cewa a wasu lokutan zabuka ka iya zama guba ga tsarin demokradiyya, domin ana samun yawan kasashen Afirka Kudu da Sahara dake gudanar da zabuka amma sau tari wadannan zabuka na kara rura wutar rikice-rikice ne maimakon maganinsu.

"A bayan nan an gudanar da muhimman zabuka a kasashe biyu. Na farko a Mali mai fama da rikici sai kuma a Zimbabwe. Yayin da aka kwatanta zaben Mali da cewa yayi nasara, amma an tabka magudi lokacin sake zaben shugaba Robert Mugabe na Zimbabwe. Ko dai wani hali ne ake ciki, a cikin shekarun baya bayan nan dai yankin Afirka Kudu da Sahara na kara zama wani yanki mai shirya zabuka ta bin tsarin demokradiyya. Sai dai duk da haka zabuka kadai ba sa nufin demokradiyyar ta wanzu musamman idan manufar demokradiyya ta wuce wani tsarin mulki na masu rinjaye a kan marasa rinjaye. A da yawa daga cikin kasashen Afirka da ake yawaita gudanar da zabe ana kwan gaba kwan baya tsakanin demokradiyya da mulkin kama karya. Wasu lokutan zabuka a kasashen rikici suke haddasawa saboda fatali da hakkin jama'a."

epa03838997 (FILE) A file photo dated 03 June 2013 shows Liberian students sitting the West Afican Examinations Council (WAEC) exams at G.W. Gibson High School in Monrovia, Liberia. The WAEC is a regional examination board which standardizes pe-university assessment and procedures in West Africa. Media reports say 27 August 2013, that all of the around 25,000 students who took the entrance exams for the University of Liberia were failed. EPA/AHMED JALLANZO *** Local Caption *** 50858767
Hoto: picture-alliance/dpa

Rashin sanin tabbas ga makomar dalibai

Daliban Laberiya ba su cancanci shiga jami'a ba inji jaridar Frankfurter Allgemeine Zeitung tana mai cewa fatan samun karin ilimi ga dalibai dubu 25 dake da niyar shiga jami'a a Laberiya ya gushe tun kafin ma su fara. Domin dukkansu sun fadi jarrabawar neman shiga jami'ar kasar. Ministar ilimin kasar da ta bayanna wannan faduwar daliban da wani kisan kare dangi da aka yi wa ilimi, ta ce za ta shiga tattaunawa da jami'ar don samun mafita.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Umaru Aliyu