1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Yuwuwar rikici gabanin zaben Guinea

Suleiman Babayo
September 24, 2020

Jagoran 'yan adawa na kasar Guinea ya yi gargadin samun rikici na kabilanci bayan wasu kalaman Shugaban kasar.

https://p.dw.com/p/3ixpM
Guinea Protest in Conakry
Hoto: AFP/C. Binani

Jagoran 'yan adawa na kasar Guinea Conakry, Cellou Dalein Diallo ya zargi Shugaba Alpha Conde da neman tayar da rikici tsakanin kabilun kasar, abin da ka iya jefa kasar kasadar fadawa a yakin basasa. Kamalan jagoran 'yan adawa sun biyo bayan wata sanarwa ta fadar shugaban kasa da ke neman goyon baya na kabilanci gabanin zaben watan Oktoba.

Shugaba Conde dan shekaru 82 da haihuwa ya yi gyara ga kundin tsarin mulkin kasar domin samun wa'adi na uku na mulki, lamarin da ya jefa kasar cikin rudanin siyasa.