1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin siyasar Masar na daukan sabon salo

August 11, 2013

Gwamnatin Masar na shirin daukar matakin tarwatsa masu zanga-zangar goyan bayan hambararren shugaban kasa Mohamad Mursi

https://p.dw.com/p/19Njp
Supporters of Egypt's ousted President Mohammed Morsi shout slogans under his posters following Friday prayers in Nahda square, where protesters installed their camp near Cairo University in Giza, southwest of Cairo, Egypt, Friday, Aug. 9, 2013. Protesters demand Morsi's reinstatement, restoration of the suspended constitution drafted under Morsi and the return of his Islamist-dominated legislative council which was also disbanded. The Arabic on the posters reads, "No for coup." (AP Photo/Amr Nabil)
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Akwai yiwuwar gwamnatin wucin gadin kasar Masar da ke samun goyon bayan rundunar soja, za ta fara aikin kawar da magoya bayan hambararren Shugaba Mohamed Mursi, wadanda suke zaman durshen tun lokacin da sojoji suka yi juyin mulki.

Wasu majiyoyin tsaro da kuma na gwamnati sun ce, mai yiwuwa da sanfin safiyar wannan Litinin jami'an tsaro za su yi dirar mikiya kan magoya bayan hambararen shugaban.

Kuma ana daukan matakan kaucewa zubar da jini, yayin fito-na-fita da ake saran zai wakana.

Masu zanga-zanga suna neman ganin an dawo da Shugaba Mursi kan madafun ikon kasar ta Masar, saboda juyin mulkin da sojoji suka yi wa zababben shugaban ya saba ka'ida.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Yahouza Sadissou Madobi