1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ruto ya ƙi amsa zargin ingiza rikici a Kenya

September 10, 2013

Mataimakin shugaban ƙasar Kenya William Ruto wanda ke fiskantar shari'a a kotun ICC dake birnin Hague ya nisanta kansa daga zargin haddasa tashe-tashen hankulan da ya hallaka fiye da mutane 1000

https://p.dw.com/p/19fba
Kenya's Deputy President William Ruto ( R) reacts as he sits in the courtroom before his trial at the International Criminal Court (ICC) in The Hague September 10, 2013. Ruto appeared at the International Criminal Court on Tuesday for the opening of his trial on charges of co-orchestrating a post-election bloodbath five years ago. Ruto and his co-accused, the broadcaster Joshua arap Sang, could face long prison terms if convicted. To the left is defense counsel Karim Khan. REUTERS/Michael Kooren (NETHERLANDS - Tags: ELECTIONS POLITICS CRIME LAW)
Hoto: Reuters

Mataimakin shugaban ƙasar Kenya William Ruto ya ƙi amsa zargin da ake masa na tafka manyan laifukan yaƙi a shari'ar da yake fuskanta a Kotun hukunta miyagun laifukan yaƙin na ICC dake birnin La Hague. Wannan shari'a dai na janyo fargaba a zukatan mutanen Kenya da ke gida, waɗanda ke ganin mai yiwuwa shariar ta sake tayar da rikicin siyasa makamancin wanda ya afku a shekarar 2007.

Babbar mai shigar da ƙara a kotun na ICC ke nan Fatou Bensouda take cewa: "Masu shari'a, hujjojin da masu shigar da ƙara zasu gabatar, zasu tabbatar muku da cewa laifukan da ake zargin Mr Ruto da Mr Sang da aikatawa, ba wai an tabka sune haka nan ba, a 'a an ɗauki lokaci ne aka shirya aka aiwatar da shi da burin ƙuntatawa magoya bayan jami'yyar PNU"

William Ruto da Joshua Sang wanda ake tuhumarsu tare na fiskantar zargin haddasa tashe-tashen hankula, bayan zaɓe shekaru biyar da suka wuce, inda suka haɗa baki da wasu su kashe mutane da dama, suka kuma tasa ƙeyar magoya bayan jami'yyun da ke hammaya da su a ƙasar Kenya.

Prosecutor Fatou Bensouda of the International Criminal Court (ICC) attends a news conference before the trial of Kenya's Deputy President William Ruto and Joshua arap Sang in The Hague September 9, 2013. REUTERS/Michael Kooren (NETHERLANDS - Tags: CRIME LAW HEADSHOT POLITICS)
Fatou BensoudaHoto: Reuters

Hujjojin mai shigar da ƙara

A jawabin buɗe shari'ar da ta yi mai shigar da ƙara a Kotun na ICC Fatou Bensouda, ta haƙiƙance cewa a cigaba da shari'ar, kuma ta yi gargadin cewa an tsorata wasu shaidu an kuma bai wa wasu cin hanci

Babban burin Mr Ruto shi ne ƙwatar iko wa kansa da jamiyyarsa, ta yin amfani da ƙarfin tuwo, kuma hakan ya kasance ne saboda ya gaza yin haka ta hanyar samun kuri'un jama'a

Wannan ne karon farko da wani babban ɗan siyasan da ke mulki zai kasance a kotu domin fiskantar shari'a ta ƙasa da ƙasa, ana ma sa ran cewa shugaban ƙasar Kenya Uhuru Kenyatta abokin hammayar William Ruto a baya wanda kuma shi ne mataimakinsa yanzu shi ma zai gurfana a gaban kotun domin amsa zargi makamancin na Ruton daga farkon watan Nuwamba idan Allah ya kai mu. Kotun dai ya cika maƙil da 'yan majalisan Kenya da iyalan William Ruto waɗanda suka kwashi jiki suka bi shi har kotun dan nuna masa goyon baya.

Kenya's Deputy President William Ruto speaks with broadcaster Joshua arap Sang (R) in the courtroom before their trial at the International Criminal Court (ICC) in The Hague September 10, 2013. Ruto appeared at the International Criminal Court on Tuesday for the opening of his trial on charges of co-orchestrating a post-election bloodbath five years ago. Ruto and his co-accused, the broadcaster Joshua arap Sang, could face long prison terms if convicted. To the left is defense counsel Karim Khan. REUTERS/Michael Kooren (NETHERLANDS - Tags: CIVIL UNREST POLITICS CRIME LAW)
Hoto: Reuters

Gardamar masu kare William Ruto

Sai dai Kharin Khan Lauyan William Ruto ya ce wata rana zaa ƙaddamar da binciken da zai duba dalilin da ya sa aka ɗorawa Ruto wannan laifin babu gaira babu dalili saboda ko a yanzu akwai ƙarancin shaidu a shari'ar

Ya yi kamar mutane da yawa na da burin samun hujjoji ko ta halin ƙaƙa, ko da ma basu dace ba, domin kawai a sami Ruto da laifi, kuma idan aka yi la'akari da abin da ɓangaren masu shigar da ƙaran ke gabatarwa, ya kamata a yi la'akari da cewa shaidu daga shiddan da babban mai shigar da ƙara Luis Moreno Ocampo ya gabatar ranar 15 ga watan Disemban shekarar 2010, uku daga cikinsu sun riga sun faɗi

Wannan shari'a dai ya raba ra'ayoyin mutane gida biyu da waɗanda ke cewa hujjojin da za a bayar a kotu ka iya tayar da ɓacin ran da aka kama hanyar mantawa da shi, da kuma waɗanda ke cewa wannan shari'a na zaman zakarar gwajin dafi na Kotun na ICC wanda har yanzu ya gaza yin nasara a sharioinsu kuma take fuskantar zargin cewa ta fi mayar da hankali kan ƙasashen Afirka a maimaikon sauran ƙasashen duniya.

Ƙorafin waɗanda abin da shafa

Lauyan da ke wakiltar waɗanda abin ya shafa Wilfred Nderitu ya ce an yaye musu mutuncinsu kuma suna cigaba da rayuwa cikin barazana da tsoro..

A dalilin haka ku masu shari'a kuke da alhakin gudanar da aiki mafi wahala, na tabbatar da cewa an gudanar da bincike kan janyewar waɗanda ake zargi da waɗanda abin ya shafa daga shari'ar, ku kuma ɗauki matakan da suka dace, waɗanda nake wakilta na da ra'ayin cewa idan har kuka yi haka, zaku ƙara ƙimar ku a idanunsu, shi sa duk da irin koma bayan da ake samu a wannan shari'a, waɗanda abun ya shafa suke kallonku da kyakyawar fata, na cewa, zaku kamanta adalci a wannan shari'a

Defence Counsel for Joshua arap Sang, Joseph Kipchumba Kigen-Katwa (C), attends a news conference before the trial of Kenya's Deputy President William Ruto and Sang at the International Criminal Court (ICC) in The Hague September 9, 2013. REUTERS/Michael Kooren (NETHERLANDS - Tags: POLITICS CRIME LAW)
Lauyan Joseph SangHoto: Reuters

Abin jira a gani dai shi ne yadda zata kaya a wannan shari'a kasancewar duk mutane 18 da kotun ta taɓa yankewa hukunci 'yan Afirka ne.

Mawallafiya: Pinaɗo Abdu Waba
Edita: Mohammad Awal Balarabe

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani