1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon Gangamin adawa a Togo

Zainab Mohammed Abubakar
December 3, 2017

'Yan adawa sun gudanar da zanga zanga a birnin Lome, boren da ke zama na ukun irinsa cikin tsukin wannan mako, a cigaba da neman shugaba Faure Gnassingbe, ya yi murabus daga kujerar shugabanci.

https://p.dw.com/p/2oft6
Togo Demonstration Togo
Hoto: picture-alliance/dpa/A.Obafemi

Mutumin da ya mulki Togo na tsawon shekaru 15 Gnassinbe dai, ya yi alkawarin tattaunawa da kungiyoyin 'yan adawa a watan Nuwamban da ya gabata,  tattaunawar da har yanzu bai kaddamar ba makonni bayan alkawarin.

Masu shiga tsakani na yankin yammacin Afirka da suka hadar da shugaban Ghana  Nana Akufo-Addo  da takwaransa na Gini  Alpha Conde, sun sha kokarin ganin an bude wannan tattaunawar ta da ci tura kawo yanzu.

Tun a shekara ta 2005 ne da Gnassingbe ya dare kujerar shugabancin kasar ta Togo biyo bayan mutuwar mahaifinsa Janar Gnassingbe Eyadema, wanda ya mulki kasar tsawon shekaru 38.