1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon gumurzu a kasar Syria

July 17, 2017

Fada ya sake kazanta tsakanin mayakan tawaye da ke da goyon bayan gwamnatin Turkiyya da kuma mayakan Kurdawa bayan arangama tsakanin bangarorin biyu a yankin arewa maso yammacin kasar Syria.

https://p.dw.com/p/2gh3d
Syrien | Aufnahmen des Kriegsfotografen Karam al-Masri
Hoto: Getty Images/AFP/K. al-Masri

Rahotanni sun ce an fafata tsakanin bangarorin biyu ne kusa da wani sansanin mayakan saman Syria a kauyen An-Dakna da ke arewacin birnin Aleppo.

Kungiyar sa ido da kare hakkin jama'a a Syria ta Syrian Observatory for Human Rights mai mazauni a Birtaniya, ta ce dakarun kasar Turkiya sun ja daga a wasu wurare da ke kewayen yankin da rikici ya faru a wannan Litinin.

Wasu sojojin gwamnatin Syriar sun ce an halaka wasu daga cikin 'yan tawayen da ke da goyon bayan kasa Turkiyya a arangamar.