Zaben Benin Magoya bayan shugaban kasar na kan gaba
May 2, 2015Talla
Hukumar zaben Jamhuriyar ta Benin da ke yankin yammacin Afirka ta sanar da cewa jam'iyyar da ke goyon bayan Shugaba Thomas Boni Yayi da ke kan karagar mulki, tana kan gaba inda ta lashe kujerun majalisar dokokin 32 daga cikin 83. Sai dai hakan na nuni da cewa jam'iyyar ta gaza samun kaso hudu cikin biyar mafi rinjaye da ka iya bai wa Shugaba Yayi damar yi wa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima. 'Yan adawar kasar dai na zargi Buni Yayi da kokarin yin gyaran fuskar domin ya dauwama a kan karagar mulki, zargin da ya musanta yana mai kara jadda aniyarsa ta sauka daga kan karagar mulki da zarar wa'adin mulkin nasa ya cika a shekara mai zuwa.