1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sakamakon zaben Najeriya kai tsaye

Ahmed SalisuMarch 30, 2015

Hukumar zaben Najeriya mai zaman kanta INEC na kan tattara sakamakon zaben shugaban kasa da ya gudana a ranar Asabar din da ta gabata.

https://p.dw.com/p/1Ezgm
Nigeria - nominierter Präsidentschaftskandidat Muhammadu Buhari und Goodluck Jonathan
Hoto: U. Ekpei/AFP/Getty Images / AP Photo

Daga sakamakon da aka bayyana ya zuwa yanzu dai Shugaba Goodluck Jonathan na jam'iyyar PDP ya yi nasara a jihohin da suka hada da Ekiti da Enugu da Abuja da Nassarawa.

Shi kuwa Janar Buhari Muhammadu Buhari mai ritaya ya samu nasara a jihohin da suka hada da Kogi da Osun da Ogun da Ondo da Oyo.