1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bude makarantu a Saliyo

February 4, 2015

Kasar Saliyo da ke zaman daya daga cikin kasar da cutar Ebola mai saurin kisa tafi kamari ta bayyana cewa za a sake bude makarantun kasar a ranar 30 ga watan Maris mai zuwa.

https://p.dw.com/p/1EVb8
Hoto: DW/J. Kanubah

Makarantun na Saliyo dai sun kwashe tsahon watanni bakwai a rufe sakamakon barkewar annobar cutar ta Ebola mai saurin kisa a yankin yammacin Afirka. Gwamnatin ta Saliyo ta dauki matakin rufe makarantun ne domin dakile yaduwar cutar ta Ebola wadda ake saurin daukarta ta hanyar cudanyar jama'a. Tun a watan Yulin shekarar da ta gabata ta 2014 ne dai mahukuntan na Saliyo suka sanya dokar ta baci a kasar biyo bayan barkewar cutar wadda ta hallaka akalla mutane 9,000 a yankin yammacin Afirka kuma 3,000 daga cikinsu 'yan kasar ta Saliyo ne.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Umaru Aliyu