1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Saudiya za ta yi amfani da sojojin kasa a rikicin Yemen

Suleiman BabayoApril 21, 2015

Saudiya za ta yi amfani da sojojin kasa a rikicin Yemen yayin da rikcin kasar ta Yemen rincabewa

https://p.dw.com/p/1FC1U
Jemen Luftangriff auf Sanaa
Hoto: Reuters/K. Abdullah

Sarki Salman na kasar Saudiya ya ba da umurnin wa dakarun musamman su shirya domin kai farmaki ta kasa kan mayakan 'yan tawayen Houthi na kasar Yemen, kamar yadda kamfanin dillancin labaran kasar ya ruwaito. Kasar ta Saudiya ke jagatantar hare-hare ta sama da ake kai wa kan mayakan na 'yan tawayen Houthi.

Kawo yanzu babu wani tabbaci kan lokacin da dakarun na Saudiya za su kutsa cikin kasar ta Yemen, da yadda za su shiga cikin rikicin.

Mayakan na Houthi da ke saman tallafin kasar Iran suna fafatawa da dakarun da ke biyayya wa Shugaba Abd Rabu Mansour Hadi na kasar Yemen, abin da ya yi sanadiyar hallaka mutane masu yawa, yayin da wasu daruruwa suka samu raunika.