1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Bashar al-Assad ya ce yana yaƙi da 'yan Al-Qaida

September 19, 2013

Shugaban na Siriya ya ce ƙasarsa ba ta cikin halin yaƙi ya ce tana fuskantar farmaki ne daga 'yan ta'adda da ke neman tayar da zaune tsaye.

https://p.dw.com/p/19kQB
Syria's president Bashar al-Assad gestures during an interview with French daily Le Figaro in Damascus in this handout distributed by Syria's national news agency SANA on September 2, 2013. REUTERS/SANA/Handout (SYRIA - Tags: CONFLICT CIVIL UNREST POLITICS ) ATTENTION EDITORS - THIS IMAGE WAS PROVIDED BY A THIRD PARTY. FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS PICTURE IS DISTRIBUTED EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS
Hoto: Reuters

Assad ya bayyana haka ne a cikin wata Hira da gidan telbijan na Amirka FOXNEWS ya yi da shi. kafin daga bisani ya musunta sahihanci aikin bincike da sefetocin Majalisar Ɗinkin Duniya suka yi a kan zargin da ake yi cewar dakarunsa sun yi amfani da makamai masu guba a kusa da birnin Damascus a cikin watan jiya a faɗan da suke yi da 'yan tawayen.

Shugaban na Siriya ya ce a shirye yake a lalata makaman nasa masu guba amma ya ce abune da ke buƙatar kuɗi kana kuma zai ɗauki lokaci sannan ya ce idan Amirka za ta iya ta biya kuɗaɗen aikin. Yanzu haka dai ana ci gaba da samun rashin zutuwa a kan batun na Siriya tsakanin sauran ƙasashen duniya da Rasha wacce ke ɗora alhakin kai hare-haren a kan 'yan tawaye.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu