1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mali: Shugaban ECOWAS ya gana da gwamnatin rikon kwarya

Abdoulaye Mamane Amadou
October 11, 2020

Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo da ke jagorantar kungiyar ECOWAS ya sauka Bamako kasar Mali a karon farko bayan dage wa Mali takunkumi sakamakon juyin mulki.

https://p.dw.com/p/3jlbY
Ghana ECOWAS | Nana Akufo-Addo
Hoto: AFP/N. Dennis

Shugaban ECOWAS ya samu tarabar shuzgaban rikon kwarya  Bah N'daw a filin jirgi, kana ya kuma gana da mataimakin shugaban kasar Assimi Goita wanda ya jagoranci kifar da gwamnatrin tsohon shugaban Ibrahim Boukar Keita a watan Agusta.

Kungiyar raya tattalin arzikin yammacin aksashen Afirka ECOWAS ko CEDEAO sun dage takunkumi karya tattalin arzikin Mali bayan da sojiojin da suka kifar da mulkin suka amince da maida kasar karkashin mulkin farar hula zuwa lokacin shirya sabon zabe, tare da yarjejeniyar sake wadanda aka kama loakcin juyin mulkin.