1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Ghana zai yi rantsuwar fara aiki

January 7, 2013

A wannan Litinin ake rantsar da Shugaban Ghana John Dramani Mahama, domin fara sabon wa'adin mulki duk da kalubalantar sakamakon zaben da bangaren adawa ke yi.

https://p.dw.com/p/17F1D
Ghana's Vice-President John Dramani Mahama (C) sits after taking the oath of office as head of state, hours after the announcement of the death of Ghana's President John Atta Mills, in the capital Accra, July 24, 2012. Mills, who won international praise for presiding over a stable model democracy in Africa, died suddenly on Tuesday and his vice-president was quickly sworn in to replace him at the helm of the oil, gold and cocoa producer. Mahama, 53, will serve as caretaker president until the elections at the end of the year. REUTERS/Yaw Bibini (GHANA - Tags: POLITICS ELECTIONS TPX IMAGES OF THE DAY)
Hoto: Reuters

A wannan Litinin ake rantsar da Shugaban Ghana John Dramani Mahama, domin fara sabon wa'adin mulki, sakamakon lashe zaben watan jiya na Disamba da ya yi.Cikin watan Juli Mahama ya zama shugaba na riko, bayan mutuwar Marigayi Shugaba Farfesa John Attah Mills ta kwatsam. Kuma tuni shugaban ya yi kirar neman hadin kai, sakamakon yadda babban dan takaran jam'iyyar adawa Nana Akufo-Addo, ke kalubalantar sakamakon zaben.

A birnin Accra fadar gwamnatin kasar, cikin wani biki ake sa ran Shugaba Dramani Mahama zai yi rantsuwar ta fara sabon wa'adin mulki na shekaru hudu.Kasar ta Ghana da ke yankin yammacin Afirka, ana yaba mata saboda kwanciyar hankali ta fuskan siyasa da ake samu.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe