1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugabannin Turayyar Turai sun amince da zabtare kasafin kudi

February 8, 2013

Shugabannin kasashen kungiyar Tarayyar Turai sun amince da zabtare kasafin kudin kungiyar da kashi uku cikin 100

https://p.dw.com/p/17bDi
Germany's Chancellor Angela Merkel (L), European Parliament President Martin Schulz (C) and France's President Francois Hollande (R) attend an European Union leaders summit meeting to discuss the European Union's long-term budget in Brussels February 7, 2013. European Union leaders begin two days of talks on a long-term budget on Thursday, with efforts to refocus spending on growth likely to be thwarted by demands for farm subsidies as pressure to reach a deal grows. REUTERS/Yves Herman (BELGIUM - Tags: POLITICS BUSINESS)
Hoto: Reuters

A wannan Jumma'a, Shugabannin kasashen kungiyar Tarayyar Turai sun amince da zabtare kasafin kudin kungiyar da kashi uku cikin 100, abun da ke zama karo na farko da su ka amince da irin wannan mataki cikin shekaru 60 da su ka gabata.

Yayin taron kungiyar wanda ke gudana a birnin Brussels na kasar Belgium, shuganannin tabbatar da cimma wannan matsaya, bayan tattaunawa ta tsawon lokaci tsakanin Firaministan Birtaniya David Cameron da goyon Shugaban gwamnatin Jamus Angela Merkel.

Matakin zabtare zai fara aiki daga kasafin kudin kungiyar na gaba na shekara ta 2014 zuwa 2020. Tuni shugabannin kasashe na kungiyar su ka nuna gamsuwa da cimma wannan matsaya. Firaministan Birtaniya David Cameron da shugaban Faransa Francois Hollande su ka fara yin maraba da matakin. Shugaban hukumar gudanar kungiyar ta Tarayyar Turai Herman Van Rompuy ya nami majalisar dokokin kungiyar ta yi abun da ya dace wajen amince da kasafin kudin, bayan cimma matsayin shugabannin kasashen kungiyar 27.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Umaru Aliyu