1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Mali sun karɓi iko da garin Ménaka.

February 12, 2013

Haɗin gwiwar sojojijn Mali da na Faransa sun shiga garin na Ménaka da ke a yankin arewaci kan iyaka da Niger ba tare da yin wani faɗa ba.

https://p.dw.com/p/17d6u
Les marsouins du 2eme RIMA accompagnent les soldat Nigerien dans leurs patrouilles pedestre et en véhicule dans la ville de GAO. Ils rencontrent la population et recueillent des informations sur la vie du village.Un dtachement de Liaison et d'assistance armé par le 2eme RIMA au profit de la MISMA accompagne depuis Niamey des éléménts de l'armée Nigerienne venue à GAO participer à la sécurisation. Les Nigerien sont aussi accompagnés par des éléments des EFS qui les ont formés dans leur pays.
Hoto: picture-alliance/CITYPRESS24

Wani babban habsan soji na Mali kanal Alaji Ag Agamu ya shaida cewar su ne da sojojin Faransa ke riƙe da garin tun sao'i 48 da suka wucce.Ya kuma ce kafin su isa a garin, mayaƙan ƙungiyar yan tawaye na MNLA sun arce, sannan kuma ya ce sun kama wasu dakarun ƙungiyar guda uku.

Tun a ranar biyar ga watan Febrairu bradan na ƙungiyar ta MNLA suke a garin na Ménaka wanda da farko ke cikin hannu masu kishin addini kafin su ficce.Wannan shi ne gari na kusan biyar da sojojin Faransa da na Mali suka karɓe daga hannu yan tawayen.Yanzu haka sojojin ƙasashen sun ƙara ƙarfafa matakan tsaro ta hanyar gudanar da bincike a kan jama'a masu yin shigi da fuci.

Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Mohammad Nasiru Awal