1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Najeriya sun kashe 'yan Boko Haram

September 7, 2013

Rundunar sojojin Tarrayar Najeriya ta sanar da cewar ta kashe mayaƙan ƙungiyar Boko Haram guda 50 a wani samame da ta kai ta ƙasa da jiragen sama na yaƙi.

https://p.dw.com/p/19dPU
A soldier sits atop an armored personnel carrier in Maiduguri, Nigeria, on Wednesday, June 5, 2013. On Wednesday, the military flew foreign and local journalists from Nigeria's capital, Abuja, to Maiduguri in Borno state as part of a tour of one battleground area. (AP Photo/Jon Gambrell)
Hoto: picture-alliance/AP

Wani kakakin rundunar, Sagir Musa a garin Maiduguri fadar gwamnatin jihar Borno ya shaida wa 'yan jaridu cewar, sojojin sun kai farmakin ne, ga maɓoya ta ƙarshe inda 'yan ƙungiyar suka ja da'ga a jihar ta Borno da ke zama cibiyarsu.

A ranar Alhamis da ta gabata (05. 09. 13), wasu mutane ɗauke da makamai waɗanda aka ce mayaƙan ƙungiyar ne ta Boko Haram sun kashe mutane guda15 a sa'ilin da suka buɗe wuta a cikin wata kasuwa da ke a garin Gajiram a yankin arewaci na ƙasar. Rundunar ta ce ' yan ƙungiyar na kai hare-haren ne na ɗaukar fansa a kan farar hula a yankin arewa maso gabashi na ƙasar.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Saleh Umar Saleh