1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Sudan ya karyata zargin da ake masa

Zulaiha Abubakar SB
January 20, 2019

'Yan sanda a Sudan sun harba hayaki mai saka hawaye kan masu zanga-zanga yayin da suka kutsa zauren majalisar dokoki da ke birnin Omdurman al'amarin da ya fusata 'yan ba ruwan mu.

https://p.dw.com/p/3BsDp
Sudan Khartum Proteste gegen Präsident Al-Baschir
Hoto: Reuters/M.N. Abdallah

Dama dai kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta zargi jami'an tsaron kasar da amfani da karfi kan masu zanga-zangar duk kuwa da cewar Shugaba Omar al-Bashir ya dora alhakin wadanda suka rasa rayukansu kan bata garin da ya ce sun fake da zanga-zanar don jefa kasar cikin rudani yayin da ya halarci wani gangami a birnin Al-Kurreda. Sabuwar zanga-zangar ta balle yayin da ma'aikatu dabam-dabam da kuma kungiyoyin Likitoci da Lauyoyi da masu hada magunguna suka tsunduma yajin aiki.

A daya bangaren Shugaba al-Bashir wanda ya dare kan madafun iko ta hanyar juyin mulki shekaru 30 da suka gabata na ci gaba da jaddada akwatin zabe a matsayin hanyar canza gwamnati a kasar.