1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikici a zauren majalisar dokokin sudan ta Kudu

Zulaiha Abubakar
June 20, 2019

Wasu daga cikin 'yan majalisar dokokin Sudan ta Kudu sun fice daga taron gabatar da kasafin kudin kasar a daidai lokacin da ministan kudin yake tsaka da bayani. Rashin biyan albashin ma'aikata ne ya haifar da sabanin.

https://p.dw.com/p/3Klxb
Sudan, Khartoum: 
Präsident des Südsudan Salva Kiir Mayarditund Oppositionsführer des Südsudan Riek Machar
Hoto: picture-alliance/M. Hjaj

A lokacin da suke yi wa maneman labarai karin haske game da ficewar tasu, 'yan majalisar sun bayyana rashin biyan albashin ma'aikata da sojojin kasar a matsayin dalilin da ya sanya su yin bore. Sun kuma bayyana yadda sojojin kasar a yanzu suka rungumi sare bishiyoyi don sayar da itace a matsayin hanyar da suke samun kudin shiga.

Tuni dai kakakin majalisar ya sanar da dage zaman majalisar zuwa wani lokaci don yin duba game da korafin 'yan majalisar. Tun a watan Mayun da ya gabata ne bangaren gudanarwar kasar da kuma jam'iyyun adawa suka amince da karin watanni shida kafin kaddamar da gwamnatin hadaka a wani bangaren cimma yarjejeniyar zaman lafiya a kasar ta sudan ta Kudu.