1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tababa game da ikirarin nasara a Mali

February 7, 2013

Sojojin Faransa na farautar 'yan tawayen da suka saje da al'ummar birnin Gao na Mali, bayan harin da wasu mayaka suka kaiwa dakarun.

https://p.dw.com/p/17aTY
French special forces drive through the city of Gao, Northern Mali, Wednesday Jan. 30, 2013. Islamist extremists fled the city Saturday after French, Chadian and Nigerien troops arrived, ending 10 months of radical islamic control over the city.(Foto:Jerome Delay/AP/dapd)
Hoto: dapd

Dakarun Faransa da ke yankin arewacin Mali na farautar 'yan tawayen da mai yiwuwa suka saje da al'ummar birnin Gao, bayan bata-kashin daya gudana kusa da birnin, wanda ya aza ayar tambaya game da ikirarin da Faransar ta yi na kwace iko da birnin.

Kakakin sojin Faransa a Mali Kanal, Thierry Burkhard ya fadi - a wanna Alhamis cewar, har yanzu suna gudanar da samamen kwace iko da birnin, furucin da kuma ke zuwa kimanin makonni biyu bayan da dakarun Faransa da na Mali suka shiga cikin birnin. Burkhard, ya fadi a birnin Paris na Faransa cewar, akwai hatsarin yiwuwar masu kaddamar da farmaki na cudanya da mazauna birnin na Gao.

A dai ranar Talatar da ta gabata ce wasu mahara suka harba makamai masu linzami akan sojojin Faransa kusa da birnin na Gao. Idan za'a iya tunawa dai a ranar 11 ga watan Janairu ne dakarun Faransa suka kaddamar da samame da nufin tallafawa sojojin Mali sake kwace iko da arewacin kasar, wanda masu kishin addini suka yi tsawon watanni tara suna gudanar da mulki a ciki.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Halima Balaraba Abbas