1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taraba: An shawo kan rikicin garin Wukari

Gazali Abdou tasawaNovember 8, 2015

Sao'i bayan sanar da hukuncin kotun zabe na cewar Senata Aishatu Jummai Alhasan ce ta lashe zaben gwamnan jihar Taraba ne, fada ya barke a garin Wukari.

https://p.dw.com/p/1H1ty
Symbolbild Gewalt in Nigeria
Hoto: SEYLLOU DIALLO/AFP/Getty Images

Rahotanni daga Wukari na jihar Taraba na cewa wata tarzoma ta barke a garin tun a daren jiya jim kadan bayan da wani hukunci kotu ya ce Senata Aisha Alhasan ce ta lashe zaben gwamna a jihar. Wakilin DW a Yola Muntaqa Ahiwa wanda ya isa a cikin jihar ta Taraba, ya ruwaito cewa wasu daga cikin mutanen garin sun tabbatar masa da cewa, da tsakar daren jiya an ji harbe-harben bindigogi.

Wannan rikici dai ya yi sanadiyyar rayukan mutane, da kawo yanzu babu cikakken adadi, daura da asarar dukiyoyi sakamakon ko-konen da aka ayi.

Sai dai ya ce ya zuwa safiyar wannan Lahadi kura ta lafa bayan da aka kai jami'an tsaro a garin.