1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron ministoci a Berlin a kan Ukraine

Yusuf BalaJanuary 9, 2015

Ministocin sun amince za su gana da juna a ranar ta Litinin mai zuwa a babban birnin Jamus a kokarin da ake yi na kama bakin zaren warware rikicin gabashin kasar Ukraine.

https://p.dw.com/p/1EI9s
Konferenz Europäische Erinnerungskulturen 2014 Frank-Walter Steinmeier
Hoto: Institut für Auslandsbeziehungen / Dietmar Gust

Ministocin harkokin wajen Faransa da Jamus da Rasha da Ukraine za su gana a birnin Berlin fadar gwamnatin kasar Jamus a ranar Litinin inda za su tattauna kan rikicin gabashin Ukraine, da aiwatar da shirin yarjejeniyar birnin Minsk.

A wata tattaunawar zauren hadaka ta wayar tarho ministocin sun amince su gana a kokarin da ake na ganin an kama bakin warware rikicin gabashin kasar ta Ukraine kamar yadda ministan harkokin wajen Jamus Frank-Walter Steinmeier ya bayyana.

Minista Steinmeier Ya ce a wannan rana za su sake zama don ganin an warware matsalolin da suka dabaibaye rikicin kasar ta Ukraine. Sai dai akwai gargada da za a iya fiskanta a hanyar da ake bi wajen ganin an aiwatar da cikakkiyar yarjejeniyar da aka kulla ta birnin na Minsk.