1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron shugabannin kasashen Kungiyar IGAD

Abdourahamane HassaneAugust 4, 2016

Shugabannin kasashe na yankin Gabashin Afirka na Kungiyar IGAD za su gudanar da wani taro a gobe Juma'a a birnin Addis Ababa na Habasha domin tattauna rikicin Sudan ta Kudu.

https://p.dw.com/p/1JbqU
Südsudan Präsident Salva Kiir und Vizepräsident Riek Machar
Hoto: picture-alliance/dpa/P. Dhil

An shirya shugabannin za su tattauna batun tura wata runduna ta musammun a Sudan ta Kudu domin tabbartar da zaman lafiya, bayan tashin hankali na baya-baya nan da ya barke a kasar tsakanin dakarun gwamnatrin na Salva Kiir da kuma na tsohon mataimakin shugaban kasar Riek Machar.Tun a shekara ta 2013 kasar ta Sudan ta Kudu take fama da yaki basassa wanda ya yi sanadiyyar mutuwar gomai na dubban rayukan jama'a