1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron yaki da ta'addanci a Afirka a Nairobi

Binta Aliyu Zurmi
July 10, 2019

Babban Magatakardan MDD Antonio Guterres ya bayyana cewa rundunar G5 Sahel ba ta da kafin da za ta iya kawar da kungiyoyin 'yan ta'adda a yakin yammacin Afirka ita kadai. 

https://p.dw.com/p/3LsML
UN-Generalsekretär Antonio Guterres
Hoto: picture-alliance/AA/A. Ozdil

Babban Magatakardan Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya bayyana hakan ne a wannan Laraba a jawabin bude babban taron yaki da ta'addanci a Afirka a birnin Nairobin kasar Kenya inda ya ce wannan matsala ta faro daga kasar Mali ta yadu zuwa kasashen Nijar da burkina Faso, da kuma sannu a hankali ke yaduwa zuwa kasashen Ghana da Togo da Cote d'Ivoire. 

Sai dai Guterres a shirye yake ya kawo goyon bayansa ga duk wani shiri da shugabannin nahiyar za su fito da shi na yakar ta'addanci a nahiyar baki daya. Guterres ya kuma nuna rashin jin dadinsa kan yadda ya kasa sanya kungiyar ta G5 Sahel a karkashin ikon Majalisar Dinkin Duniya kamar yadda kasashe mambobin kungiyar suka bukata sau tari.