1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Makomar Siriya a siyasance

Yusuf BalaDecember 26, 2015

An dai daura damba ta ganin shirin tattaunawar zaman lafiya ta dore kan makomar Siriya inda Majalisar Dinkin Duniya za ta zauna a Geneva a watan Janairu mai zuwa.

https://p.dw.com/p/1HU5n
Staffan de Mistura / Syrien / UN
Staffan de MisturaHoto: picture-alliance/AA

Jakadan Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan harkokin Siriya Staffan de Mistura ya bayyana fata da ke akwai na shiga tattaunawa da bangarori masu gaba da juna a kasar Siriya, wato bangaren shugaba Bashar al-Assad da bangaren 'yan adawa tun daga ranar 25 ga watan Janairu a Geneva kamar yadda ofishin jakadan ya bayyana a ranar Asabar din nan.

A cewar jawabin da ke fitowa daga ofishin na De Mistura ana kara azama kan duk wasu matakai da za su kai ga wannan tattaunawa a wannan rana da aka tsara tare da neman hadin kan dukkanin bangarorin, sannan jawabin ya kara da cewa ba za a yi sakaci ba shirin da aka fara samun ci gaba a kansa na tattaunawar sulhu ya fiskanci wata matsala.