'Yan gudun hijira a Najeriya na cikin halin tsaka mai wuya bayan da suka tsere daga garin Gwoza na jihar Borno domin gujewa hare-haren Boko Haram mai gwagwarmaya da makamai a kasar. Kungiyar nan ta "Bring Back Our Girls" ce dai ta ce ta gano 'yan gududn hijirar a garin Kubura da ke daf da Abuja babban birnin Tarayyar Najeriyar.