1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Girka na shirin tsuke bakin aljihu

Lateefa Mustapha Ja'afarJuly 15, 2015

Firaministan kasar Girka Alexis Tsipras na ci gaba da fuskantar kalubale daga 'ya'yan jam'iyyarsa ta Syriza gabanin kada kuri'ar amincewa da matakan tsuke bakin aljihu.

https://p.dw.com/p/1FyyC
Firaministan Girka Alexis Tsipras
Firaministan Girka Alexis TsiprasHoto: Reuters

Majalisar dokokin kasar ta Girka ce dai za ta kada kuri'ar amincewa da sabbin matakan na tsuke bakin aljihu da gwamnatin Tsipras ta dauka wanda alamu ke nuni da cewa sai dai ya nemi goyon bayan 'yan jam'iyyar adawa kasancewar zai yi wahala 'ya'yan tasa jam'iyyar su kada kuri'ar amincewa. Tuni dai mataimakiyar ministan kudi Nadia Valavani ta ajiye mukaminta, inda ta ce ba za ta iya cin amanar bukatar da al'ummar kasar suka nuna ta yin watsi da matakan tsuke bakin aljihun yayin kuri'ar raba gardama ba. A wani labarin kuma kungiyar kwadagon kasar ta nuna kin amincewarta da matakan na tsuke bakin aljihu da Firaminista Tsipras ya amince da su tare kuma da kiran yajin aiki na tsahon sa'oi 24 a baki dayan ma'aikatun gwamnatin kasar domin nuna adawarta.