1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsohon jami'in lafiya ya halaka mutane 100 a Jamus

Yusuf Bala Nayaya
October 30, 2018

Tsohon ma'aikacin jinyar nan da ake zargi da kisan marasa lafiya100 ya amince a wannan Talata cewa ya aikata wannan muguwar ta'asa da ke zama mafi kazanta a tarihin Jamus tun bayan lokacin yakin duniya na biyu.

https://p.dw.com/p/37Nvk
Deutschland Prozess gegen Krankenpfleger Niels Högel
Hoto: picture-alliance/dpa/J. Stratenschulte

Alkali mai shari'a a arewacin birnin Oldenburg Sebastian Buehrmann ya tambayi Niels Hoegel ko ya amince da zarge-zargen da ake masa na kisan marasa lafiyar? Sai ya ce "haka ne abin da ya aikata kenan" kamar yadda Hoegel dan shekaru 41 ya bayyana a gaban kotu.Tshohon ma'aikacin jinyar dai ya rika ba da magunguna fiye da kima ga marasa lafiyar.

Mai gabatar da karar ya ce babban burin bude sauraren karar shi ne samar da haske cikin duhu kan irin ta'asar da ta dauki lokaci ana aikatawa a wasu asibitoci biyu na kasar ta Jamus don kaucewa gaba.