Jirgin mai suna F16 ya sami nasarar dakatar jirgin Rasha
October 5, 2015Talla
Ta cikin sanarwar data fitar mahukuntan Turkiyyan sun gayyaci jakadan Rasha dake a birnin Ankara zuwa ma’aikatar harkokin wajen Turkiyan a inda suka nuna rashin jin dadin su kan kutsen da jirgin Rashan yayi a sararin samaniyar kasar.
Sanarwar ta kara da cewar muddin aka kara kwatawa to Rashan baza taji da dadi ba.
Tun dai a ranar asabar din nan ce jirgin Rashan yayi kutse a sararin samaniyar Turkiya da misalign karfe 9 a gogon GMT a kudancin lardin Yayladagi ata cewar ma’aikatar harkokin wajen Turkiyyan.
Tuni dai ministan harkokin wajen Turkiyan ya kira takwaran san na Rasha Sergei Lavrov don nanata masa damuwar mahukuntan kasar kan kutsan jirgin na Rasha.