1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Warware rikicin Kongo na fuskantar tarnaƙi

November 26, 2012

'Yan tawayen M23 sun yi watsi da sharaɗin gwamnatin Kinshasa na janyewa daga Goma kamin hawa teburin shawara

https://p.dw.com/p/16pt5
M23 rebel group political leader Bishop Jean Marie Runiga is escoted after giving a press conference on July 11, 2012 in Bunagana. DR Congo authorities and the United Nations fear that the M23 movement, which took one town on the Uganda border last week and forced 600 government troops to flee, may target the provincial capital of Goma, UN officials said yesterday. M23, a group of mutineers, has already briefly taken other towns near its new stronghold in Bunagana. AFP PHOTO/Michele Sibiloni (Photo credit should read MICHELE SIBILONI/AFP/GettyImages)
Jean Marie Runiga shugaban ƙungiyar tawayen M23Hoto: Michele Sibiloni/AFP/GettyImages

A ƙarshen makon da ya gabata ne shugabanin ƙasashen Yuganda,Kenya, Tanzaniya da na Jamhuriya Demokraɗiyar Kongo su ka shirya taron ƙoli na mussamman a birnin Kamapla na ƙasar Yuganda, tare da halartar ƙungiyar gamayyar Afrika, inda suka tattana game da halin da ake ciki a rikicin da ya ɓarke tsakanin gwamnatin Jamhuriya Demokraɗiyar Kongo da 'yan tawayen M23, da suka mamaye birnin Goma da wasu yankunan na gabacin Kongo.

Shugabanin sun ba 'yan tawayen M23 wa'adin kwanaki biyu, domin su fice daga Goma sannan kuma su shiga tattanawa da gwamnatin Kinshasa domin warware rikicin cikin ruwan sanhi.

Yau ne wa'adin ƙarshe da taron shugabanin ya ba 'yan rawaye na ficewa daga Goma: A yau din sun fiddo sanarwa inda suka ba su ga wata takarda ba arubuce daga Kampafa wadda ta bukaci sunjanye daga GOma.

Game da batun tattanawa da gwamnatin Kinshasa kuwa,gwamnatin Joseph Kabila ta ce ba za ta hau tebirin shwara da ƙungiyar M23 ba, sai lokacin da ta fita daga Goma, sharaɗin da shugaban ƙungiyar tawayen M23 Jean-Mari Runiga Lugero ya sa ƙafa ya shure:

Congolese flee the eastern Congolese town of Sake , 27kms west of Goma, Friday Nov. 23 2012. Thousands fled the M23 controlled town as platoons of rebels were making their way across the hills from Sake to the next major town of Minova, where the Congolese army was believed to be regrouping. The militants seeking to overthrow the government vowed to push forward despite mounting international pressure.(Foto:Jerome Delay/AP/dapd)
Hoto: AP

"Ba ta kamata janyewa daga birnin Goma ta zama sharaɗin tattanawa tare da mu ba, kamata ta yi a ce ta zama sakamakon shawararin sulhun idan dai da niyar cimma sulhun.Idai aka ce sai mun fita dag Goma, to yaudararmu ce a ke so ayi.Sannan mu fita daga Goma mu tafi ina.?

Jean-Mari Runiga Lugero ya musanta zargin da ake na cewar suna samun ɗaurin gindi daga ƙasar Ruwanda, ya kuma bada dalilan da suka sa ƙungiyar M23 ta shiga gwagwarmaya da gwamnatin Kinshasa:

"Ba da san mune ba mu ka ɗauki makamai, buƙatarmu itace gwamnatin Kongo ta fahinci cewar kasa ta fada cikin matsaloli ta fannoni daban-daban, siyasa tattalin arziki da rayuwar jama'a ta yau da kullum.Sannan mu na so gwamnati ta fahinci cewar burinmu shine warware wannan matsaloli ta hanyar sulhu, saboda haka a shirye mu ke mu hau tebirin shawara da ita, amma ba tare da gitta sharaɗi ba."

A yayin da ake fama da cece-kuce game da tattanawar sulhu jama'a da yaƙin ya rutsa da su na fama cikin uƙuba.Wasu rahotani da ƙungiyar kare haƙƙoƙin bani Adama ta ƙasa da ƙasa wato Human Right Wach da kuma Majalisar Dinkin Duniya suka gabatar sun zargi 'yan tawayen M23 da gallazawa jama'a a yankunan da suka mamaye, zargin da shugaban ƙungiyar ya musanta:

" Al'ummomin da ke zaune a yankin su da kansu suka ƙaryata wannan rahotani.Sun hito sun shirya zanga-zanga, inda suka danganta rahotani da sharri domin ɓata sunan M23.Rundunoninmu sun ƙunshi sojoji da 'yan sanda masu biyyaya, wanda ke aiki dare da rana, domin kare lafiyar jama'a da dukiyoyinsu".

Rwandan President Paul Kagame (L), his counterparts Yoweri Museveni (C) of Uganda and Joseph Kabila (R) of the Democratic Republic of Congo's (DRC) attend on November 21, 2012 a summit meeting at the Speke Resort in the Kampala suburb of Munyonyo. The leaders of the Democratic Republic of Congo, Rwanda and Uganda said on November 21 that the M23 rebels who have seized the eastern Congolese town of Goma must pull out immediately. The United Nations accuses Rwanda of backing M23 fighters who now control Goma, charges Kigali denies. Uganda has also dismissed charges it has aided the rebels. AFP PHOTO / PETER BUSOMOKE (Photo credit should read PETER BUSOMOKE/AFP/Getty Images)
Kagame, Museveni da KabilaHoto: Peter Busomoke/AFP/Getty Images

A yau ma za a cigaba da tattanawa a birnin Kampala na ƙasar Yuganda tsakanin shugaban rundunar ƙasar da na ƙungiyar tawayen M23.sannan a nata gefe itama ƙungiyar Gamayyar Afrika ta kiri taron na musamman a wannan Litinin, game da rikicin Jamhuriya Demokraɗiyar Kongo.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Mohammad Nasiru Awal

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani