1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wasu jami'an gwamnatin Najeriya sun mutu a hatsarin jirgin sama

December 16, 2012

Gwamnan jihar Kaduna Patrik Ibarhim Yakowa da wasu muƙarrabansa sun rasu, a hatsarin jirgin sama cikin jihar Bayalsa

https://p.dw.com/p/173Kd
The wreckage of a plane burns in Nigeria's commercial capital Lagos, June 3, 2012. A plane that crashed into a downtown area of the Nigerian city Lagos on Sunday had 147 people on board, a source at the national emergency management agency said. The source said the aircraft belonged to privately owned domestic carrier Dana Air. Two sources at Lagos airport also said the number on board was around 150. REUTERS/Stringer (NIGERIA - Tags: DISASTER TRANSPORT) QUALITY FROM SOURCE
Hoto: Reuters

Gwamnan jihar kaduna da ke a yankin arewacin Tarrayar Najeriya Patrick Ibrahim Yakowa da tsohon mai bai wa shugaban ƙasar shawara a kan al'amuran tsaro janar Azazi Allah ya yi masu cikawa a wani hatsarin jirgin sama da ya auku.

Hukumomi sun ce mutane a ƙalla guda shidda suka mutu a cikin hatsarin da wani jirgin saman soji mai saukar ungulu ya yi da su a jihar Bayalsa. Shugaban ƙasar ta Najeriya ya ba da ummarnin da a gudanar da binciken gaggawa domin gano dalilan hatsari. Wannan dai shi ne karo kusan na barkatai da ake fama da hatsarin jirgin sama a Najeriyar, wanda a cikin sa a kan samu asaran rayukan jama'a.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane

Edita : Usman Shehu Usman