1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wata Kotu a Indiya ta hukunta masu laifin aikata fyaɗe

August 31, 2013

Kotun ta yanke ma wani matashi mai shekaru 17 da haihuwa hukuncin ɗaurin shekaru uku na zama gidan yari, bayan da ta same shi da laifin aikata fyaɗe a kan wata mata mai shekaru 23.

https://p.dw.com/p/19ZWy
Indian policemen escort the juvenile (C, in pink hood), accused in the December 2012 gang-rape of a student, to a court in New Delhi on August 31, 2013. A New Delhi court is due to hand down its verdict August 31 in the case of a teenager accused of taking part in the fatal gang-rape of a student, which sparked outrage across the country. AFP PHOTO/Prakash SINGH (Photo credit should read PRAKASH SINGH/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

Shi dai wannan matashin ya na ɗaya daga cikin gungun mutane da suka sace matar a cikin motar safa a birnin Delhi tare da yi mata fyaɗen da ya yi sanadin sheƙawarta lahira.

Ana ci gaba da gudanar da shari'ar sauran waɗanda ake zargin da su da laifin waɗanda suka mallaki hankalin kansu. Bisa ga dokokin ƙasar ta Indiya dai, za a iya yanke ma waɗannan mutane huɗu hukucin kisa idan aka same su da laifi. Tuni ma dai ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi da laifin fyaɗen ya rigaya ya rataye kansa a gidan yari. Wannan fyaɗen dai ya janyo tofin Allah tsine daga sassa daban-daban na Indiya, inda waɗanda suka gudanar da zanga-zanga game da wannan batu suka yi kira da a rataye waɗanda suka aikata fyaɗen.

Mawallafi : Mouhamadou Awal Balarabe
Edita : Abdourahamane Hassane