1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yajin aikin gama gari a Ethiopiya

Abdourahamane Hassane BAS
March 5, 2018

A birnin Addis Ababa na Ethiopiya shaguna da kantuna da makaratun sun kasance a rufe a sakamakon yajin aikin gama gari da kungiyoyin masu fafutuka da na 'yan siyasa suka kira domin nuna damuwa da dokar ta baci.

https://p.dw.com/p/2tjz8
Ethiopia State of Emergency Merkel (picture alliance / AP Photo)
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Daga cikin yankunan da yajin aikin ya fi samu karbuwa har da yankin 'yan kabilar Oromo kabila mafi rinjaye a kasar, kana masu adawa da gwamnatin. An dai kafa dokar ta bacin ne a cikin watan da ya gabata  a jajibirin da firaminista Hailemariam Desalegn ya yi marabus. 

Zanga-zangar nuna kyamar gwamnati, da 'yan kabilar na Oromo suka soma yi tun a shekara ta 2015 zuwa 2016 ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 940.