1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yajin aikin ma'aikata ya gurgunta harkoki a Filato

December 11, 2012

Harkokin rayuwa sun tsaya cik a jihar Filato dake arewacin Najeriya sakamakon yajjin aikin gama gari da ma'aikatan jihar suka soma a ranar Talata.

https://p.dw.com/p/1707T
Protesters take to the streets of Nigeria's capital Abuja Wednesday March 31, 2010, to demand electoral reforms before the coming 2011 presidential election.The crowds demanded the current head of Nigeria's Independent National Electoral Commission not be reappointed. Abduwahid Omar, president of the Nigeria Labour Congress, told the gathered crowds that reforms must be credible if the results of next year's elections are to be taken seriously. In 2007, Nigeria saw its first civilian-to-civilian transfer of power in a nation long beset by military dictatorships. However, the election was marred by fraud, intimidation and violence. (ddp images/AP Photo/Sunday Alamba).
Hoto: dapd

Bankuna, gdajen mai, wuraren harkokin jama'a da kuma ofisoshin gwamnatin jiha da na tarayya sun kasance a kulle.

Tun da sanyin safiyar wannan Talata dai shugabannin ƙwadago a jihar Filato suka soma kewayawa zuwa ofisoshin gwamnati daban daban domin tabbatar da ganin cewar sun bi ƙa'idar shiga yajin aikin. A sa'ilin da wakilinmu a Jos Abdullahi Maidawa Kurgwi ya kewaya birnin Jos, ya tarar da 'yan ƙwadagon tare da sabon kwamishinan 'yan sandan jihar Filato Chris Olakpe a ƙofar shiga sakatariyar gwamnatin jiha, yana roƙon 'yan ƙwadagon cewar ka da yajin aikin ya kai su ga lalata dukiyoyin jama'a.

Garin na Jos na cikin matakan tsaro, haka ma labarin yake a akasarin yankunan ƙananan hukumomin jihar 17, to ko ina wannan yajin aiki ya dosa, komarade Jibrin Bancir, shine shugaban ƙungiyar ƙwadago na jihar Filato yayi ƙarin bayani, inda yace: "sun fara kenan sai duk lokacin da gwamnatin jihar Filato ta biya su kuɗin albashin su na watanni shida."

Haramtaccen yajin aiki

To sai dai kuma gwamnatin jihar ta Filato ta ce wannan yajin aiki ya saɓa ƙa'ida domin kuwa na farko bai kamata ya zama na gama gari ba, hakan nan kotu ta baiwa 'yan ƙwandagon takardar dakatar da su shiga yajin aikin kamar yadda kakakin gwamnatin jiha Yiljab Abraham ya nunar.

Titel: DW_Nigeria_Integration-online3 Schlagworte: Polizeikontrolle, Kano, Boko Haram Fotograf: Katrin Gänsler Aufnahmedatum: 05. Februar 2012 Aufnahmeort: Kano, Nigeria Bildbeschreibung: In der Stadt Kano gibt es überall Polizeikontrollen
Zirga-zirga ta ragu a kan tituna sakamakon yajin aikiHoto: Katrin Gänsler

To amma kuma shugabanin ƙwadagon suka ce ba su sami wata takarda ba daga kotu, don haka suka tsunduma yajin aikin na sai baba ta gani. Wasu daga ma'aikatan sun ce wannan shi ne matakin ƙarshe da suka ɗauka na neman hakkin su. Rahotanni daga Shendam, Langtang da wasu yankunan jihar sun ce an rufe hanyoyin mota, shaguna, da ofishoshin gwamnati don nuna biyayya ga wannan umurni da ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa da bada, da zummar ganin cewar gwamnatin jihar Filato ta bai wa ma'aikatan yankunan hukumomin hakkokin su.

Mawallafi: Abdullahi Maidawa Kurgwi
Edita: Mohammad Nasiru Awal

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani