1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yakar fashin teku a Afirka

October 27, 2013

Shugabannin yammaci da tsakiyar Afirka sun ce sun dau aniyar hada hannu waje guda domin yakar fashin da ke cigaba da karuwa a mashiga a kogin Gini.

https://p.dw.com/p/1A6sN
(FILE) A file photograph dated 30 January 2007 shows Nigerian militants patroling in the creeks of the Niger delta region of Southern Nigeria. Three French crewmen have been kidnapped in an attack on a ship in an oilfield off the coast of Nigeria on 21 September 2010. Marine services company Bourbon claims pirates in several speedboats attacked one of its vessels. There has been no claims of responsibility but kidnappings and attacks are frequent in the Niger Delta, the heart of Africa's biggest oil and gas industry. EPA/GEORGE ESIRI
Masu fashin teku da ke addabar tsakiya da yammacin AfirkaHoto: picture-alliance/dpa

Shugabannin sun ambata hakan ne yayin da suka fara wani taro a ranar Asabar a kasar Senegal inda suka ce za su tashi tsaye wajen warware wannan matsala ta fashin teku da ma ta'addanci a yankunan.

Wannan taro na ranar Asabar dai ya biyo bayan makamancinsa da aka gudanar a kasar Kamaru a cikin watan Yunin da ya gabata wanda ya fidda wasu dabaru na yakar fashin tekun bayan da kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya bukaci da a yi hakan.

Fashin na teku a mashigar kogin na Gini dai na jawo asarar miliyoyin daloli ga 'yan kasuwa da ma dai gwamnatoci.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammad Nasiru Awal