1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan sandan Masar sun kashe 'yan bindiga

Abdul-raheem Hassan
December 24, 2017

'Yan sandan Masar sun dauki fansa a kan 'yan bindiga da ake zargi da yawan kai hare-haren ta'addanci a yankin Sinai inda suka yi nasarar kashe mutane tara daga cikin 'yan ta'addan.

https://p.dw.com/p/2puGs
Ägypten Cairo - Ägyptische Polzizeieinheiten bewachen den Tahrir Platz in Kairo
Hoto: Getty Images/AFP/M. El-Shahed

Rundunar 'yan sandan Masa ta tabbatar da kashe wasu 'yan bindiga tara da ake zargi da kitsa kai hare-hare a yankin Sinai da ke Arewa maso gabashin kasar. Ma'aikatar cikin gidan kasar ta ce sumamen ya biyo bayan samun labarin cewar 'yan ta'addan sun kafa sansanin horars da makaman yaki a lardin Sharqiya. 'Yan sanda sun kuma gano manyan bindigogi masu sarrafa kansu da sinadaran sarrafa bama-bamai a sansanin 'yan ta'addan.

Dama dai ana zargin gungun 'yan bindiga da suka tare a gandun dajin Sharqiya da alhakin hare-hare a kan ofisoshin 'yan sanda da jami'an soji, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar jami'an tsaro da dama a yankin Sinai.

Tun dai bayan wani mummunan hari da ya kashe mutane sama da 300 a masallacin Jumma'a watannin baya, Shugaban kasar Masar Abdel Fatah al-Sisi ya umarci jami'an tsaro da su murkushe ayyukan ta'addanci a kasar cikin watanni uku.