1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cutar tamowa na barazana ga yaran Habasha

Ramatu Garba Baba
August 10, 2021

Daruruwan yara kanana na fuskantar barazanar yunwa da cutar tamowa a sakamakon rikicin yankunan Afar da Tigray da ke kara kamari a Habasha.

https://p.dw.com/p/3ymHc
Symbolbild Hunger Übersättigung Ungleiche Verteilung von Lebensmitteln
Hoto: Michael Gottschalk/photothek/imago images

UNICEF ta baiyana damuwarta kan barazanar yunwa da yara kanana ke fuskanta a kasar Habasha, yara kimanin miliyan hudu ne za su fuskanci tsananin yunwa a sakamakon kazancewar fada a yankin Afar da Tigray, ta nemi bangarorin biyu, da su dakatar da fadan don ceto rayukan wadannan yaran.

Daga cikin wasu sama da dubu dari hudu da rikici ya raba da muhallansu, akwai yara da dama da iyayensu suka yi gudun hijira da su, da ke fama da cutar tamowa inji Unicef.