1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotun ICC za ta bude bincike a Najeriya

December 11, 2020

Kotun binciken manyan laifuffuka ta ICC ta ce ta mallaki shedu da dama kan kashe-kashen da 'yan kungiyar Boko Haram ke yi a Najeriya.

https://p.dw.com/p/3mbSH
Niederlande Den Haag | ICC | Internationaler Strafgerichtshof
Hoto: Everett Collection/picture alliance

Babbar mai shigar da kara a kotun hukunta masu aikata manyan laifuffuka ta kasa da kasa wato ICC Fatou Bensouda, ta ce tana da cikakkiyar shedar fara bincike kan kashe-kashen da masu ikirarin jihadi ke yi a arewa maso gabacin Najeriya.

Mai shigar da karar ta kara da cewa shedun da ke gareta a hannu, sun isa a bude bincike kan abin da ke gudana a yankin na arewacin kasar.

Kungiyar Boko Haram ta kwashe sama da shekaru goma tana kisan farar hula da basu ji ba basu gani ba a jihohin Barno da Yobe.

Yankin arewacin na Najeriya na cigaba da fuskantar hare-haren 'yan ta'ada da masu garkuwa da mutane.