1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a sake zama kan shirin nukiliyar Iran

Yusuf BalaJuly 7, 2015

Shirin nukiliyar ta Iran mai cike da cece ku ce, ana son tsaida shi aƙalla tsawon shekaru goma kafin sassauta takunkumin tattalin arziki da aka sanya wa Iran.

https://p.dw.com/p/1FumG
Wien - Atomgespräche mit dem Iran
Mahalarta taron nukiliyar IranHoto: picture alliance/AA

Sakataren harkokin wajen Birtaniya Philiph Hammond ya bayyana cewar zai sake komawa kan tattaunawar da ake yi kan shirin nukiliyar Iran a Vienna a daren gobe Laraba, sannan manyan ƙasashen da ke cikin wannan tattaunawa ana sa ran su sake zama a ranar Alhamis. Mista Hammond ya fada wa manema labarai cewar a daren gobe Laraba za su tabbatar da tattauna abubuwa da dama kafin ranar Alhamis su cimma matsaya

Ƙasar ta Iran da manyan ƙasashen duniya shida masu karfin fada aji Birtaniya da China da Faransa da Jamus da Rasha da Amirka na duba matsaya da za su cimma kan shirin nukiliyar ta Iran mai cike da cece ku ce, da ake son tsaidawa aƙalla tsawon shekaru goma kafin sassauta takunkumin tattalin arziki da aka ƙaƙabawa ƙasar ta Iran.